Yan Boko Haram Sun Sace Wasu Mata A Cikin Kasar Kamaru
Yan kungiyar Boko Haram sun sace wasu mata biyar a kauyen Tolkomari da ke shiyar Arewa mai nisa a Jamhuriyar Kamaru.
Mahukunta a kauyen Tolkomari da ke kasar Kamaru sun sanar da cewa; Mayakan kungiyar Boko Haram sun yi awungaba da wasu mata biyar da suke aiki a gonar albasa a kauyen na Tolkomari da ke lardin Mayo-Sava a shiyar arewa mai nisa a Jamhuriyar Kamaru a jiya Talata.
A bayan sace matan biyar shugabannin gargajiya a kauyen na Tolkomari sun bukaci shugaban kasar Kamaru Paul Biya da ya ba su izinin yin amfani da maita da tsafi a fagen yaki da mayakan kungiyar Boko Haram domin kubuta daga hare-haren wuce gona da irin ‘yan kungiyar da a halin yanzu haka suka janyo hasarar dubban rayukan mutane da sace mata da yara.