An Gano Kaburburan Gama Gari Guda Hudu A Kasar Libya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i24535-an_gano_kaburburan_gama_gari_guda_hudu_a_kasar_libya
Majiyar yansanda a birnin Bengazi na kasar Libya ta bayyana cewa yansandan sun gano wasu kabururruka guda hudu na gama gari wadanda suke dauke da gawawwaki kimani 80.
(last modified 2018-08-22T11:30:46+00:00 )
Oct 01, 2017 19:18 UTC
  • An Gano Kaburburan Gama Gari Guda Hudu A Kasar Libya

Majiyar yansanda a birnin Bengazi na kasar Libya ta bayyana cewa yansandan sun gano wasu kabururruka guda hudu na gama gari wadanda suke dauke da gawawwaki kimani 80.

Kamfanin dillancin labaran Anatolio ya nakalto jami'an yansanda na Bengazi suna bada wannan sanarwan a yau Lahadi, sun kuma kara da cewa tuni an bukaci wata tawagar likitoci ta ziyarci wurin don gano masu gawawwakin.

Majiyar ta kara da cewa kungiyar yan ta'adda ta Ansarusshari'a ce ta taba iko da yankin a baya, don haka mai yuwa ita ce ta kashe wadan nan mutane ta kuma bisne su a can. 

A shekarar da ta gabata ma an gano wani kabarin gama gari a wannan yankin dauke da gawawwaki kimani 72 .