Kamaru : Yaki Da Boko Haram, Ya Tsananta Talauci_ Crisis Group
Oct 25, 2017 07:49 UTC
Kungiyar International Crisis Group, dake nazari kan rikice rikice a duniya, ta fitar da wani rahoto dake cewa yakin da ake da kungiyar Boko haram ya tsananta talauci matuka a yankin arewa mai nisa na kasar Kamaru.
A rahoton data fitar kungitar ta (ICG), ta ce tun kafin zuwan Boko haram da ma yakin yana cikin tsaka mai wuya saboda talauci, aman yakin da aka shiga da kungiyar a 2014 ya kara tsananta lamarin.
Kungiyar ta bukaci da a samar da wani shiri na farfado da tattalin arzkin yankin cikin gaggawa.
Yankin arewa mai nisa na Kamaru ya kunshi yawan al'umma da ya kai miliyan hudu.
Tags