Libya: An Kashe Sojojin Gwamnati Uku A Yankin Banighazi
Nov 07, 2017 06:27 UTC
Sojojin sun mutu ne a sanadiyyar fadan da suka yi da 'yan ta'adda a ckikin birnin na Banighazi da ke gabacin kasar ta Libya.
Kamfanin dillancin labarun Xinhua na kasar Sin ya ambato wata sanarwa ta sojojin kasar a jiya litinin na tabbatar da mutuwar sojojin uku.
Kasar Libya ta tsunduma cikin rikici ne tun a shekarar 2011 da kungiyar yarjejeniyar tsaro ta Nato ta kifar da gwamnatin Mu'ammar Khaddafi.
Da akwai kungiyoyin masu dauke da makamai a kowace kusurwar kasar da suke fada a tsakaninsu akan madafan iko da kuma man fetur.
A gabacin kasar da akwai kungiyoyi masu alaka da kungiyoyin 'yan ta'adda na al'ka'ida da Da'esh.
Tags