Libya: An Kashe Sojoji Biyu A Fada Da 'Yan ta'adda
Dec 04, 2017 18:48 UTC
Kakakin sojojin gwamnatin Libya ne ya sanar da kashe sojojin kasar a fada da 'yan ta'adda a yankin Banighazi.
Kamfanin dillancin labarun Xinhua ya kuma ambato kakanin sojan na Libya Milud al-zawy, yana ci gaba da cewa; Sojojin suna ci gaba da fada da yan ta'addar da su ke a gabacin kasar.
Banighazi da ke gabacin Libya yana a matsayin yankin da 'yan ta'adda su ka yi dandazo, tun bayan faduwar gwamnatin Khaddafi a 2011.
Janar Halifa Hatfar wanda yake samun goyon bayan wasu kasashen larabawa ya bude yaki akan kungiyoyin 'yan ta'adda shekaru uku kenan a jere.
Tags