Kotun Daukaka Kara Ta Wanke Dan Rahoton RFI
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i26599-kotun_daukaka_kara_ta_wanke_dan_rahoton_rfi
kotun daukaka kara ta sojin Kamaru ta wanke wakilin sashen Hausa na radiyon France International RFI Ahmad Abba daga dukkanin zarge-zargen da ake masa.
(last modified 2019-08-10T10:24:46+00:00 )
Dec 22, 2017 08:38 UTC
  • Kotun Daukaka Kara Ta Wanke Dan Rahoton RFI

kotun daukaka kara ta sojin Kamaru ta wanke wakilin sashen Hausa na radiyon France International RFI Ahmad Abba daga dukkanin zarge-zargen da ake masa.

Tun a watan Yulin shekarar 2015 ne, jami'an tsaro suka kama Ahmad Abba a yankin Maroua da ke arewacin kasar ta Kamaru lokacin da yake hada wani rahoto da ya shafi kungiyar Boko Haram.

Bayan gurfanar da Ahmad Abba gaban kotu  a wancan lokaci aka yanke masa hukuncin daurin shekaru 10 a gidan kan zargin da ake yi masa na halasta kudaden haram da kuma gudanar da ayyukan ta'addanci. To sai dai kuma bayan daukaka kara, a Safiyar jiya Alhamis,  Kotun daukaka kara ta Sojin da ke zama a birnin Yaounde ta wanke Ahmad Abba tare da rage hukuncin zuwa daurin watanni 24 a gidan yari.

Hukuncin kotun  ya nuna cewa Ahmad Abba wanda ya shafe tsawon watanni 29 a gidan kaso, ya kammala wa'adin da aka yanke masa.