Libya : Ana Tattaunawa A Oman Kan kundin Tsarin Mulki
-
tutar libya
Kwamitin shirya kundin tsarin mulkin kasar Libya ya fara gudanar da wani taro tattaunawa a birnin Salalah dake kudancin kasar Oman kan kundin tsarin mulki na farko da za a samar a kasar, tun bayan hambarar da mulkin tsohon shugaban kasar Muammar Ghaddafi.
Ana gudanar da tattaunawar ce bisa shiga tsakanin tawagar MDD mai kula da aikin tallafawa kasar Libya, wanda ya samu halartar wasu membobin kwamitin shirya kundin tsarin mulkin Libyan.
Za a kwashe kwanaki ana gudanar da taron, kuma mahalarta taron za su tattauna wasu batutuwa don cimma matsaya guda a kansu.
Kwamitin ya kunshi membobi 55, sai dai wasu daga cikinsu basu halarci taron ba a wannan karo, sakamakon rashin gamsuwa kan ayyukan da aka tanada wajen shirya kundin tsarin mulkin kasar.
Kwamitin shirya kundin tsarin mulkin na Libya, ya fara gudanar da taronsa na farko a watan Afrilun shekarar 2014, da niyyar samar da daftarin tsarin mulki cikin kwanaki 120, sa'an nan za a gabatarwa jama'ar kasar, domin su kada kuri'ar raba gardama don zartas da kundin.
Amma sakamakon yakin da ya-ki-ci-ya-ki-cinyewa a kasar, har yanzu ba a kammala aikin samar da daftarin kundin tsarin mulki a kasar ba.