Janar Khalifa Haftar Ya Jaddada Muhimmancin Gudanar Da Zabuka A Kasar Libiya
Babban kwamnadar rundunar sojin Libiya da ke gabashin kasar Janar Khalifa Haftar ya jaddada muhimmancin gudanar da zabukan 'yan Majalisun Dokokin Libiya bayan gudanar da dukkanin shirye-shiryen da suka dace.
A jawabinsa kan bukatar gudanar da zabuka a Libiya: Babban kwamandan rundunar sojin Libiya da ke gabashin kasar Janar Khalifa Haftar ya bayyana cewa: Dole ne kafin batun gudanar da zabukan 'yan Majalisun Dokokin Kasar a samu daidaiton baki a tsakanin jami'an Libiya kan kundin tsarin mulkin kasar.
Khalifa Haftar ya kara da cewa: Samun daidaito baki a tsakanin jami'an Libiya shi ne matakin farko da zai kawo karshen duk wasu tashe-tashen hankula da suke kai ga zubar da jini a kasar.
Tun a shekara ta 2011 Libiya ta tsunduma cikin rikicin yake-yake tsakanin kungiyoyi bayan da kasashen yammacin Turai da Amurka suka kaddamar da yaki kan kasar tare da kashe shugabanta Mu'ammar Gaddafi, inda a halin yanzu ake da gwamnatoci biyu a kasar ta Libiya.