MDD Za Ta Binciki Jirgin Ruwa Mai Makare Da Abubuwan Fashewa
Manzon mUsamman na MDD a kasar Libya, Gassan Salamah, ya ce; Majalisar za ta aike da kwararru domin yin bincike akan jirgin ruwan kasar Turkiya mai makare da abubuwa masu fashewa
Gassan Salamah wanda ya yi rubutu a shafinsa na Twitter ya ci gaba da cewa; Kasar Libya tana da bukatuwa da zaman lafiya da tsaro, kuma da akwai kudurin Majalisar Dinkin Duniya wanda ya hana shigar da makamai kasar.
A ranar asabar da ta gabata ne dai gwamnatin kasar Girka ta sanar da tsaida wani jirgin ruwa mai suna " Anmakare" da abubuwa masu fashewa wanda kuma mallakin kasar Turkiya ne.
Sai dai ofishin jakadancin kasar Turkiya da yake a kasar Libya ya ce; makaman da suke cikin jirgin mallakin kasar Habasha ne ba Libya ba.