Libya: Ana Samun Karuwar Fataucin Mutane
Feb 06, 2018 12:46 UTC
Majalisar Dinkin Duniya ce ta sanar da cewa ana samun kararuwar fataucin mutane a kasar Libya
Kamfanin dillancin labarun Faransa ne ya ambato wasu rahoton sirrin na binciken da kwararrun Majalisar Dinkin Duniya suka gudanar akan kasar libya, wanda kuma aka gabatar wa da mambobi 15 na kwamitin tsaro, wanda a ciki aka yi ishara da karuwar fataucin mutane.
Rahoton mai shafuka 157 ya kuma bayyana yadda take hakkin bil'adama yake karuwa a cikin Libya.
Har ila yau an ambaci yadda kungiyar Da'esh take kokarin kafa alaka da masu fatauncin mutane ta hanyar amfani da kudi.
Rashin tabbas ta fuskar tsaro a kasar Libya ya share fagen bullar fatauncin mutane da kuma sayar da bakaken fata a matsayin bayi.
Tags