An Bukaci Dakatar Da Kai Hare-Hare A Arewacin Siriya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i28255-an_bukaci_dakatar_da_kai_hare_hare_a_arewacin_siriya
Ministan harakokin wajen Jamus ya bukaci a dakatar da duk wani motsin soja a arewacin kasar Siriya
(last modified 2018-08-22T11:31:26+00:00 )
Feb 16, 2018 06:29 UTC
  • An Bukaci Dakatar Da Kai Hare-Hare A Arewacin Siriya

Ministan harakokin wajen Jamus ya bukaci a dakatar da duk wani motsin soja a arewacin kasar Siriya

Kamfanin dillancin labaran kasar Faransa ya nakalto Sigmar Gabriel ministan harakokin wajen kasar Jamus yayin taron ministocin harakokin wajen kasashen Turai da ya gudana a birnin Sofia na kasar Bulgaria a jiya Alhamis na cewa ya kamata a tabbatar an koma kan tebirin tattaunawa tsakanin gwamnatin Siriya da kuma kungiyoyin dake dauke da makamai sannan kuma a dakatar da duk hare-haren da ake kaiwa a arewacin kasar.

A nasa bangare, ministan harakokin wajen kasar Faransa Jean-Yves Le Drian ya bayyana cewa wajibi a gaggauta komawa kan tebirin tattaunawa tsakanin 'yan kasar ta Siriya bisa goyon Majalisar Dinkin Duniya.

A jiya Alhamis ne ministocin harakokin kasashen wajen Turai suka fara gudanar da taro domin tattauwa halin da kasar siriya ke ciki, musaman ma a game da yadda hukumomin kasar turkiya suka kaddamar da hare-haren kan al'ummar kurdayan kasar ta siriya a cikin 'yan kwanakin nan.

A yau juma'a ce ake san za a kamala wannan taro.