Kamaru: "Yan Aware Sun Sake Sace Wani Jami'in Gwamnati
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i28597-kamaru_yan_aware_sun_sake_sace_wani_jami'in_gwamnati
Kamfanin dillancin labarin Xinhua ya ambato majiyar gwamnatin kasar tana cewa; 'Yan awaren sun sace Nimboum Arung Jung wanda jami'i na al'amurran zamantakewa a yankin arewa maso gabacin kasar.
(last modified 2018-08-22T07:01:29+00:00 )
Feb 26, 2018 15:36 UTC
  • Kamaru:

Kamfanin dillancin labarin Xinhua ya ambato majiyar gwamnatin kasar tana cewa; 'Yan awaren sun sace Nimboum Arung Jung wanda jami'i na al'amurran zamantakewa a yankin arewa maso gabacin kasar.

Majiyar ta kara da cewa kawo ya zuwa yanzu jami'an gwamnatin yankin da aka sace sun kai biyu. A ranar 11 ga watan Febrairu ma, 'yan awaren sun sace Batibo wanda shi ma jami'in gwamnati ne a yankin masu magana da harshen Ingilishi.

Yankin da ke magana da turanci a arewa masu yammacin kasar ta Kamaru, sun shelanta kudurinsu na ballewa daga kasar domin kafa tasu kasar.

Adadin masu magana da harshen na turanci sun kai kaso 20% na jumillar al'ummar kasar mai mutane miliyan 20.