Mar 06, 2018 12:02 UTC
  • Sudan Ta Kudu Ta Maida Martani Kan Tsoma Bakin Kasashen Turai A Harkokin Kasarta

Gwamnatin Sudan ta Kudu ta bayyana cewa duk wani matakin tsoma bakin kasashen yammacin Turai a harkokin cikin gidanta musamman daukan matakan matsin lamba kanta ba zasu taimaka wajen wanzar da zaman lafiya da sulhu a kasar ba.

A taron manema labarai da ya gudanar a birnin Juba fadar mulkin kasar Sudan ta Kudu: Ministan watsa labaran kasar Michael Makuei ya bayyana cewa: Gwamnatin Sudan ta Kudu tana shirye ta koma kan kujerar tattaunawa da bangaren 'yan tawayen kasar a birnin Adis Ababa na kasar Habasha da nufin rayar da shirin neman wanzar da zaman lafiya da sulhu a kasar Sudan ta Kudu.

Makuei ya kara da cewa: Sudan ta Kudu ba zata taba lamintar matsin lamba da barazana daga bangaren kasashen yammacin Turai ba musamman kasashen Amurka da Birtaniya da suka sanyo ta gaba.  

Tags