An Kai Hari Akan Tawagar Shugaban Majalisar Koli Ta Mulkin Kasar Libya
Mar 16, 2018 06:17 UTC
Tashar talabijin din aljazera ta ambato ofishin Abdurrahamn Suwaihili yana cewa; An bude wuta akan ayarin motocinsa ne a yayin da yake ziyartar wasu garuruwa biyu da ke yammacin kasar
Sanarwar ta ci gaba da cewa; An jikkata mutane biyu da suke a cikin tawagar yayin da aka sace wasu 'yan sanda hudu.
Wannan shi ne karo na biyu da al-Suwaihili yake tsallake rijiya da baya sanadiyyar harin da ake kai masa.
A ranar 20 ga watan Febrairu na 2017 an kai wa Abdurrahman al-Suwaihili hari tare da pira ministansa Fayez al-suraj a birnin Tripoli.
Majalisar Dinkin Duniya ta yi tir da harin da aka kai wa Suwaihali tare da jaddada muhimmancin kauracewa amfani da karfi domin cimma manufofin siyasa.
Tags