Martanin MDD Kan Sace Alkarin Kotun Soja A Libiya
MDD ta bukaci a dauki matakin da ya dace na kare lafiyar alkalin kotun soja da aka yi awan gaba da shi a kasar Libiya.
Cikin wata sanarwa da suka fitar, Dakarun wanzar da zaman lafiya na MDD a kasar Libiya sun nuna damuwarsa kan sace Massoud Erhuma babban alkalin kotun soja na kasar da 'yan bindiga suka yi awan gaba da shi , tare da bayyana cewa wannan babban cikas ne ga Hukumar kasar ta Libiya.
A ranar 15 ga watan Maris din da muke ciki ne, wasu 'yan bindiga suka yi awan gaba da Massoud Erhuma babban alkalin kotun sojan kasar a kofar gidansa dake birnin Tripoli babban birnin kasar, kuma ya zuwa babu wani gungu ko kungiya da ta dauki alhakin sake shi.
A nasa bangare, kwamitin kare hakin bil-adama na kasar Libiya ya bayana lamarin da rashin mutunta magabatan shari'a a kasar, inda ya bukci a gaggauta gudanar da bincike domin hukunta wadanda suka aikata wannan laifi.