An Sauke Ministan Tsaron Kasar Libya
Jul 30, 2018 12:14 UTC
Shugaban gwamnatin hadin kan kasar ta Libya Fayez al-Siraj ne ya sanar da sauke al-Mahadi al-Barghathi daga kan mukaminsa na ministan tsaro.
Shugaban gwamnatin hadin kan kasar ta Libya ya sanar da cewa an sauke ministan tsaron ne daga kan mukaminsa saboda yana da hannu a cikin harin da aka kai wa sansanin sojan sama na Brak da ke yankin Wadi al Shati da ke yammacin kasar a ranar 18 ga watan Mayu na 2017.
A yayin wancan harin dai an kashe mutane 150 tare da jikkata wasu daruruwa.
Libya ta fada cikin rashin tsaro ne tun 2011 bayan kisan da aka yi wa mu'ammar Khaddafi.
Tags