Mar 10, 2019 15:45 UTC
  • Sudan: Albashir Ya Yi Wa Wasu Manyan Jami'an Soji Ritaya

Shugaban kasar Sudan Umar Hassan Albashir ya yi wa wasu daga cikin manyan jami'an sojin kasar ritaya.

Kamfanin dillancin labaran Anatoli ya bayar da rahoton cewa, a wani mataki da shugaban kasar Sudan Umar Hassan Albashir ya dauka  na yin garambawul a cikin rundunar sojin kasar, ya yi wa wasu daga cikin manyan jami'an sojin kasar ritaya, haka nan kuma ya kara wa wasu mukamai.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke fuskantar gagarumar zanga-zanga domin yin kira Albashir da ya sauka daga kan karagar mulki, wadda ya kwashe shekaru 30 a kanta.

Tuna  cikin watan Disamban 2018 da ta gabata ce aka fara gudanar da zanga-zangar ta Sudan, domin kokwa kan matsalolin tsadar rayuwa, daga bisani kuma ta rikide ta koma ta adawa da gwamnati.

Tags