Mayakan Boko Haram Sun Kashe Sojojin Kamaru Ukku
Apr 20, 2016 13:15 UTC
Wasu majiyoyin labarai sun bayyana cewa mayakan boko haram sun kashe sojojin
Wasu majiyoyin labarai sun bayyana cewa mayakan boko haram sun kashe sojojin Kamaru 3 sun kuma raunata wasu ukku a wani harin ba zata da suka kai masu a arewacin kasar.
Kamfanin dillancin laraban APF ya bayyana cewa harin ya auku ne a yankin Dabanga dake kan iyakar kasar ta tarayyar Nigeria.
Mayakan boko haram dai sun kashe mutane fiye da dubu 15 a arewacin Nigeria tun shekara 2009. inda a shekara ta 2015 kungiyar ta kwace iko da wasu yankuna da dama a arewa maso gabacin kasar. Kasashen Nigeria Niger Camaroo da Chadi ne suka fi fama da mayakan na boko haram a yankin.
Tags