Libya : An Kashe Sojojin Gwamnatin hadaka 32
May 19, 2016 06:41 UTC
A Libiya adadin sojojin gwamnatin hadaka na kasar da suka mutu a wani harin da aka kai da mota da kuma fafatawa da 'yan ta'adan IS ya kai 32.
Wata sanarwa da rundinar sojin ta wallaffa a shafin na twetter ta kuma ce an samu wasu sojoji 50 da suka raunana.
lamarin dai ya auku ne jiya Laraba a yankin Abou Grin dake da nisan kilomita 130 a yammacin Syrte.
tun da farko dai rundinar sojin kasar ta ce sojoji 18 ne suka rasu.
Tags