Libya: 'Yanto da kudancin garin Ajdabiya daga 'Yan ta'adda.
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i7207-libya_'yanto_da_kudancin_garin_ajdabiya_daga_'yan_ta'adda.
Sojojin Libya sun fatattaki 'yan ta'adda daga Kudancin Ajdabiya.
(last modified 2018-08-22T06:58:29+00:00 )
Jun 25, 2016 02:42 UTC
  • Libya: 'Yanto da  kudancin garin Ajdabiya daga  'Yan ta'adda.

Sojojin Libya sun fatattaki 'yan ta'adda daga Kudancin Ajdabiya.

Tashar telbijin din al-mayadden ta bada labarin cewa; Sojojin gwamnatin Hadin Kan Kasa, a karkashin jagorancin Halifah Haftar, sun kwace kudancin birnin Ajdabiya bayan fada mai tsanani a tsakaninsu da 'yan kungiyar Da'esh.

A wasu sassan na gabacin kasar kamar alqawarisha, sojojin Libyan suna samun wasu nasarorin akan 'yan ta'addar. Tuni dai sojojin su ka kwace yankin Qar-Yunus da ke a Banighazi.

Dama tun da fari, sojojin kasar su ka shiga garin Sart bayan fada mai tsanani da 'yan kungiyar Da'esh.