Libya Ta Zargi Faransa Da Keta Hurumin Kasar Ta
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i8431-libya_ta_zargi_faransa_da_keta_hurumin_kasar_ta
Gwamnatin hadaka ta Libya ta zargi Faransa da keta hurumin kasar ta, bayan sanarwar hukumomin Paris na cewa sojojinta Faransa uku sun mutu a Libya, bayan da aka harbo jirgi mai saukar ungulun da suke ciki.
(last modified 2018-08-22T06:58:37+00:00 )
Jul 21, 2016 00:56 UTC
  • Libya Ta Zargi Faransa Da Keta Hurumin Kasar Ta

Gwamnatin hadaka ta Libya ta zargi Faransa da keta hurumin kasar ta, bayan sanarwar hukumomin Paris na cewa sojojinta Faransa uku sun mutu a Libya, bayan da aka harbo jirgi mai saukar ungulun da suke ciki.

Wata sanarwa da gwamnatin Libya ta wallafa a shafin ta na facebook ta ce abun allawadai ne kuma keta hurumin kasar ne abunda faransa ta yi ba tare da wata hujja ba ko kuma amuncewar kasar.

Firayi ministan gwamnatin hadaka ta Libya Fayez al-Sarraj 

Rahotanni daga Libya sun nuna cewa daririwan mutane ne sukayi zanga-zanga a sassa daban daban na kasar don nuna kyammarsu ga kasancewar sojojin Faransa a Libya.

Da safiyar ranar Laraba ne, kakakin ma'akatar tsaron Faransan, Stephane Le Foll , a karon farko ya tabbatar da cewa dakarun Faransa na musamman sun mutu a Libya a lokacin da suke tsaka da bautawa kasa.

wani sojan faransa 

Har yanzu dai babu wata kungiya data dau alhakin kakkabo jirgin na Faransa.