Ma'aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Kalubalantar Ayyukan Ta'addanci
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i16989-ma'aikatar_harkokin_wajen_kasar_iran_ta_jaddada_wajabcin_kalubalantar_ayyukan_ta'addanci
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Dole ne a kan kasashen duniya su hada kai a fagen yaki da duk wani nau'in ayyukan ta'addanci.
(last modified 2018-08-22T06:59:35+00:00 )
Jan 25, 2017 07:10 UTC
  • Ma'aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Kalubalantar Ayyukan Ta'addanci

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Dole ne a kan kasashen duniya su hada kai a fagen yaki da duk wani nau'in ayyukan ta'addanci.

A zaman hadin gwiwa tsakaninsa da shugaban rundunar 'yan sanda bangaren yaki da muggan kwayoyi a yau Laraba: Sayyid Abbas Arakche mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: babu wata kasa ita kadai da zata samu nasarar murkushe ayyukan ta'addanci a duniya, don haka dole ne sai an samu hadin kai da taimakekkeniya a tsakanin kasashen duniya.

Har ila yau Sayyid Arakche ya jaddada samun karin hadin gwiwa tsakanin kungiyoyin kasa da kasa da Jamhuriyar Musulunci ta Iran a fagen yaki da fataucin muggan kwayoyi musamman gani yadda kasar Iran take wahala a kokarin dakile fataucin muggan kwayoyin a kan iyakokin kasarta.