Iran ce A gaba Wajen Fada Da Makaman Kare Dangi.
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i17630-iran_ce_a_gaba_wajen_fada_da_makaman_kare_dangi.
Ma'aikatar harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa; Iran ba za ta taba mancewa da hare-haren makamai masu guba da tsohon shugaban kasar Iraki, Sadam ya kawo wa al'ummar kasarta ba.
(last modified 2018-08-22T06:59:40+00:00 )
Feb 14, 2017 03:12 UTC
  • Iran ce A gaba Wajen Fada Da Makaman Kare Dangi.

Ma'aikatar harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa; Iran ba za ta taba mancewa da hare-haren makamai masu guba da tsohon shugaban kasar Iraki, Sadam ya kawo wa al'ummar kasarta ba.

Ma'aikatar harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa; Iran ba za ta taba mancewa da hare-haren makamai masu guba da tsohon shugaban kasar Iraki, Sadam ya kawo wa al'ummar kasarta ba.

Mataimakin ministan harkokin wajen Iran Sayyid Abbas Iraqche da ya ke jawabi a wurin kaddamar da wani littafi akan hare-haren makamai masu guba da Iraki ta kawo wa Iran, ya ce; Bayan wadancan hare-haren ne, duniya ta fahimci cewa wajibi ne a kawo karshen wadannan makamai da kuma hana adana su, balle kuma hana amfani da su.

Irakchi ya kara da cewa;  Dubban mutanen da su ka yi shahada da kuma zama nakasassu sanadiyyar hare-haren na makamai mai guba, suna a matsayin wani sako ne mai kargi zuwa ga duniya akan zaluncin da aka yi wa al'ummar Iran.