Sojojin Saudiyya Sun Kashe Fararen hula 17 A Kasar Yamen
Sep 16, 2016 14:26 UTC
Jiragen yakin Saudiyya Sun kashe Fararen hular Yamen 17 a yau juma'a.
A yau juma'a jiragen yakin Saudiyya sun kai hari a yankunan San'a da Ma'arib na kasar Yamen, wanda ya yi sanadin mutuwar fararen hula 17.
Tashar telbijin din al-masirah ta kasar Yamen ya bada labarin cewa; Jirgin yakin Saudiyya ya kai hari akan wata motar matafiya a yankin alotdeh a garin Kholan da ke gundumar San'aan, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 10.
Jiragen yakin na Saudiyyar sun kuma kai wani harin a yankin Wadi al-Zagan da ke garin Sarwah a gundumar Ma'arib, da ya ci rayukan mutane 5.
A garin Gorgumar ma dai jiragen yakin na Saudiyya sun kai wasu hare-haren a yau juma'a.
Tags