An Kashe Sojojin Saudiyya Da Dama A Kasar Yamen
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i12133-an_kashe_sojojin_saudiyya_da_dama_a_kasar_yamen
Jami'an Tsaron Yamen Sun Kashe Manyan Jami'an Saudiyya
(last modified 2018-08-22T06:59:03+00:00 )
Oct 08, 2016 03:24 UTC
  • An Kashe Sojojin Saudiyya Da Dama A Kasar Yamen

Jami'an Tsaron Yamen Sun Kashe Manyan Jami'an Saudiyya

Jami'an Tsaron Yamen Sun Kashe Manyan Jami'an Saudiyya a yankin Ma'arib.

Tashar Telbijin din al-masirha ta Yamen ta ambaci cewa a jiya juma'a sojoji da dakarun sa-kai, sun kai hari da manyan bindigogi a yankin Sarwah, a gundumar Ma'arib, tare da kashe jami'an sojojin Saudiyya da dama.

Daga cikin wadanda aka kashe a harin na jiya da akwai Manjo-Genar Abdurra al-shidady wanda shi ne kwamandan 'yan koren Saudiyya a Yamen.

Bugu da kari, daga cikin wadanda aka kashe da akwai Shayif al-amury da Ali al-humaisy da su ke cikin kwamandojin sojojin Yamen, yan kore.

Fiye da shekara guda kenan dai da Saudiyya ta shelanta yaki akan kasar Yamen da al'ummarta.