Halakar 'Yan Koren Saudiyya 11 A Kasar Yemen
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i15931-halakar_'yan_koren_saudiyya_11_a_kasar_yemen
A kalla 'yan koren Saudiyya 11 ne mayakan Yemen su ka kashe a yankin kudu maso yammacin kasar.
(last modified 2018-08-22T06:59:28+00:00 )
Dec 31, 2016 08:52 UTC
  • Halakar 'Yan Koren Saudiyya 11 A Kasar Yemen

A kalla 'yan koren Saudiyya 11 ne mayakan Yemen su ka kashe a yankin kudu maso yammacin kasar.

Majiyar Sojan Yemen ta ci gaba da cewa; Shida daga cikin 'yan koren Saudiyyar an kashe su ne a gabacin "Jabalul-Han' da ke yankin 'al-Dhubab' a gundumar Ta'az.

Majiyar ta ci gaba da cewa; wasu hudu daga cikin 'yan koren sun halaka ne a cikin garin 'al-salu' sai kuma mutum guda a tuddan 'al-wakil'

Manyan bindigogin sojoji da kuma mayakan sa kan kungiyar "Ansarullah' sun kai hari akan sansanin sojojin Saudiyya da ke al-huraiqah.

Tun a cikin watan Maris na 2015 ne Saudiyyar ta bude kai harin soja akan Yemen, wanda kawo ya zuwa yanzu ya ci dubban rayuka.