Sojojin Gwamnatin Yamen Suna Ci Gaba Da Murkushe Sojojin Hayar Saudiyya
Sojojin gwamnatin Yamen da dakarun sa-kai na kungiyar Ansarullahi ta mabiya Huthi suna ci gaba da murkushe sojojin kawancen Saudiyya da suke gudanar da yaki a kasar Yamen.
Rahotonni sun bayyana cewa; Sojojin Yamen da taimakon dakarun kungiyar Ansarullahi ta mabiya Huthi sun samu nasarar halaka sojojin hayar masarautar Saudiyya masu tarin yawa a lardin Ma'arib tare da jikkata wasu masu yawa a yau Alhamis.
Har ila yau dakarun sa-kai na kabilun larabawan Yamen da suke goyon bayan gwamnatin kasar sun kai hare-haren kan sansanonin sojojin hayar masarautar Saudiyya a lardin Hujjah, inda suka kashe da dama daga cikin sojojin hayar tare da fatattakan wadanda suka rage.
A gefe guda kuma jiragen saman yakin masarautar Saudiyya suna ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri kan yankuna daban daban na kasar Yamen lamarin da ke ci gaba da lashe rayukan fararen hula da suka hada da mata da kananan yara.