Sojojin Iraki Sun Kashe Jagoran Da'esh Na Biyu
Rundinar sojin Iraki ta sanar da kashe jagora na biyu na kungiyar IS (Da'esh) wato Ayad Hamid al-Jumaili, yayin wani farmaki da sojojin kasar suka kai kwanan baya a yankunan yammacin kasar.
Bayanai sun nuna cewa mutumin da aka kashe, ya zama jagora na biyu na IS, biyo bayan Abu Bakr al-Baghdadi.
Baya ga Jumaili din, akwai sauran wasu jagororin kungiyar ta IS wadanda aka kashe a yayin luguden wutan.
A halin yanzu, sojojin gwamnatin Iraki na kokarin kwace ikon birnin Mosul daga hannun IS.
Idan ana tuni a karshen watan Maris, hukumar leken asirin kasar Iraki ta ce, sojojin saman kasar sun yi luguden wuta kan maboyar 'yan ta'addan IS guda uku a garin Ba'aj dake kan iyakar kasar da Siriya, inda suka hallaka kusan 200 daga cikinsu, wadanda suka shigo Iraki daga kasar Siriyar.