Yemen: Jiragen Yakin Saudiyya Sun Kashe Fararen Hula 20
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i25083-yemen_jiragen_yakin_saudiyya_sun_kashe_fararen_hula_20
Jiragen yakin na Saudiyya sun kai hari ne akan iyakar Gamr a gundumar Sa'adah da ke arewacin kasar.
(last modified 2018-08-22T07:00:52+00:00 )
Oct 21, 2017 14:50 UTC
  • Yemen: Jiragen Yakin Saudiyya Sun Kashe Fararen Hula 20

Jiragen yakin na Saudiyya sun kai hari ne akan iyakar Gamr a gundumar Sa'adah da ke arewacin kasar.

Kamfanin dillancin labarun  "Irna" ya ambato majiyar tsaron kasar ta Yemen na cewa; Harin ya yi sanadiyyar  mutuwar fararen hula 20, yayin da wasu biyar suka jikkata.

 A arewacin birnin Sa'adah, jiragen yakin Saudiyyar sun harba makamai masu kwafsa da aka haramta amfani da su a duniya, tare da jikkata kananan yara biyar.

A jiya juma'a ma dai jiragen yakin na Saudiyya tare da sojojin hayar kasar Sudan sun kai hari a garin Medi da ke kan iyaka. Sau 20 jiragen yakin suka kai wa garin hari.

Tun a cikin watan Maris na 2015 ne dai Saudiyyar ta shelanta yaki akan al'ummar Yemen da kawo ya zuwa yanzu suka kashe fiye da mutane 12,000 bisa kididdigar Majalisar Dinkin Duniya.