Yemen: Jiragen Yakin Saudiyya Sun Kashe Fararen Hula 11
A jiya alhamis ne dai jiragen yakin Saudiyyar suka kai hare-hare a babban birnin kasar San'aa da kuma yankin Sa'adah da ke arewacin kasar.
Baya ga mutane 11 da suka rasa rayukansu, wasu 8 kuma sun jikkata.
Tun a 2015 ne dai Saudiyyar bisa cikakken goyon bayan Amurka, ta fara kai wa kasar Yemen harin soja wanda har yanzu yake ci gaba. Hare-haren na Saudiyya sun kashe mutane fiye da 13,000 bisa kididdigar Majalisar Dinkin Duniya.
A gefe daya killacewar da Kasar Saudiyyar ta yi wa Yemen ta haddasa bullar yunwa da kuma cutar kwalara wacce kawo ya zuwa yanzu mutane miliyan 1 suka kamu da ita.
Kungiyar kare hakkin bil'adama ta "Human Rights Watch" ta bukaci da a shigar da sunan yarima muhammad Bin Salman na Saudiyya cikin jerin sunayen masu aikata manyan laifukan yaki domin hukunta shi Yemen.