Wata Kotun Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan 'Yar Jamus
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i27471-wata_kotun_iraki_ta_yanke_hukuncin_kisa_kan_'yar_jamus
Wata kotu a birnin Bagadaza na Iraki ta yankewa wata 'yar asalin kasar Jamus hukuncin kisa, saboda alaka da kungiyar 'yan ta'adda ta IS.
(last modified 2018-08-22T11:31:18+00:00 )
Jan 21, 2018 10:51 UTC
  • Wata Kotun Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan 'Yar Jamus

Wata kotu a birnin Bagadaza na Iraki ta yankewa wata 'yar asalin kasar Jamus hukuncin kisa, saboda alaka da kungiyar 'yan ta'adda ta IS.

Kotun mai kula da harkokin da suka shafi ta'addanci a Iraki, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya kan matar wacce ba'a bayyana sunan ta ba.

An dai tuhumi matar ne da taimakawa kungiyar 'yan ta'addan da kayan aiki domin kai hare-hare a kasashen Siriya da Iraki, kamar yadda wata sanarwa da kakakin kotun, mai shari'a Abdel Settar Bayraqdar ya fitar a yau Lahadi.