Yemen : Harin Sama Ya Kashe Masu Bikin Aure A kalla 20
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i30210-yemen_harin_sama_ya_kashe_masu_bikin_aure_a_kalla_20
Rahotanni daga Yemen na cewa a kalla mutane 20 ne dake halartar wani bikin aure, suka gamu da ajalisu, biyo bayan wani harin sama.
(last modified 2018-08-22T11:31:44+00:00 )
Apr 23, 2018 11:09 UTC
  • Yemen : Harin Sama Ya Kashe Masu Bikin Aure A kalla 20

Rahotanni daga Yemen na cewa a kalla mutane 20 ne dake halartar wani bikin aure, suka gamu da ajalisu, biyo bayan wani harin sama.

Lamarin dai ya auke ne yammacin Jiya Lahadi a lardin Bani Qais, dake Hajja, a yankin arewa maso yammacin kasar ta Yemen, a cewar majiyoyin agaji.

Ko baya ga wadanda suka rasa rayukansu da akwai, wasu mutane 40 da aka garzaya dasu asibitin yankin sakamakon raunana da suka samu a cewar kungiyar agaji ta ''Médecins sans frontières'' a shafinta na Twitter.

Tuni dai 'yan gwagwarmayar neman sauyi na Houtsis dake rike da ikon yankin, suka danganta hare-haren ga kawancen sojin kasa da kasa da Saudiyya ke jagoranta kan yakin kasar ta Yemen.