Yemen : Yerjejeniyar Tsagaita Wuta Ta Soma Aiki
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i3730-yemen_yerjejeniyar_tsagaita_wuta_ta_soma_aiki
A kasar Yemen, a cikin daren jiya ne yarjejeniyar tsagaita wuta dake samun goyon bayan majalisar dinkin duniya ta soma aiki.
(last modified 2018-08-22T06:58:07+00:00 )
Apr 10, 2016 23:08 UTC
  • Da misalin karfe 12 na daren lahadin nan ne yerjejeniyar ta soma aiki. (hoto © ISNA)
    Da misalin karfe 12 na daren lahadin nan ne yerjejeniyar ta soma aiki. (hoto © ISNA)

A kasar Yemen, a cikin daren jiya ne yarjejeniyar tsagaita wuta dake samun goyon bayan majalisar dinkin duniya ta soma aiki.

Tsagaita wutar na zuwa ne gabanin tattaunawar zaman lafiya da za a yi ranar 18 ga wata a Koweit tsakanin dakarun gwamnati da 'yan tawayen Houthi.

MDD, ta bukaci masu rikici a kasar ta Yemen dasu mutunta yerjejeniya wace ake fatan zata kawo karshen yakin da yayi sanadin mutuwar mutane fiye da 6,000.

Wata sanarwa da mai shiga tsakani na MDD a rikicin kasar, Ismail Ould Cheikh Ahmed ya fitar gabanin tsagaita wuta ta ce wannan babban ci gaba ne a matakin dawo da zamen lafiya, tare da bada damar isar da kayan agaji ga dubban al'umma wannan kasa da suka tagaiyara sakamakon farmakin ba -gaira-ba dalili da Saudiyya ke jagoranta yau sama da shekara guda.