Ambaliyar Ruwa Da Zaftarewar Kasa Ta Kashe Mutum 22 A Indonusiya
https://parstoday.ir/ha/news/world-i33597-ambaliyar_ruwa_da_zaftarewar_kasa_ta_kashe_mutum_22_a_indonusiya
Hukumomi a yankin Sumatra dake yammacin kasar Indonusiya sun sanar da mutuwar mutane 22 biyo bayan ambaliyar ruwa da zaftarewar data biyo bayan ruwan sama da aka samu tamakar da bakin kwarya a yankin da yammacin jiya Juma'a.
(last modified 2018-10-13T11:53:09+00:00 )
Oct 13, 2018 11:53 UTC
  • Ambaliyar Ruwa Da Zaftarewar Kasa Ta Kashe Mutum 22 A Indonusiya

Hukumomi a yankin Sumatra dake yammacin kasar Indonusiya sun sanar da mutuwar mutane 22 biyo bayan ambaliyar ruwa da zaftarewar data biyo bayan ruwan sama da aka samu tamakar da bakin kwarya a yankin da yammacin jiya Juma'a.

Daga cikin wadanda suka mutun akwai dalibai na wata makarantar kwana ta Islamiya a wani kauye na lardin Mandailing Natal.

Ko baya ga wadanda suka rasa ransu akwai mutane da dama da suka bata a cewar hukumomin yankin.

Bayanan sun ce akwai gidaje da dama da suka lalace bayan wannan iftila'in.

Masu aikin ceto dai na fuskantar kalubale wajen isa a yankunan da iftila'in ya shafa saboda zaftarewar kasa a cewar shugaban hukumar agajin gaggawa na yankin.