Mutane Miliyan 10 Na Kasar Yemen Na Bukatar Taimakon Abinci
https://parstoday.ir/ha/news/world-i34401-mutane_miliyan_10_na_kasar_yemen_na_bukatar_taimakon_abinci
Majalisar Dinkin Duniya ce ta bayyana cewa mutane miliyan 10 na kasar Yemen din za su bukaci abinci a shekara mai zuwa
(last modified 2018-12-11T07:14:52+00:00 )
Dec 11, 2018 07:14 UTC
  • Mutane Miliyan 10 Na  Kasar Yemen Na Bukatar Taimakon Abinci

Majalisar Dinkin Duniya ce ta bayyana cewa mutane miliyan 10 na kasar Yemen din za su bukaci abinci a shekara mai zuwa

Mataimakin babban magatakardar Majalisar Dinkin Duniya Mark Lowcock da ya gabatar da taron manema labaru akan batun ya kara da cewa; Ana samun karuwar tabarbarewar al'amurra a kasar Yemen, don haka muna da bukatuwa da taimakon kudade

Lowcock ya ci gaba da cewa; Majalisar Dinkin Duniya tana son ganin ta samar da abinci ga mutane kasar Yemen miliyan 15 a shekara mai zuwa

Babban magatakardar Majalisar Dinkin Duniyar Antonio Gutrress ne zai jagoranci kaddamar da gidauniyar tara kudade domin al'ummar kasar Yemen a ranar 26 ga watan Febrairu na shekara mai zuwa.

Lowcock ya kuma ce ana da bukatuwa ne da kudin da za su kai dala biliya 4 saboda tanadar abinci ga al'ummar kasar ta Yemen