Kamaru : Hare-haren Kunar Bakin Wake Sun Kashe Mutane 6
https://parstoday.ir/ha/news/world-i568-kamaru_hare_haren_kunar_bakin_wake_sun_kashe_mutane_6
Akasarin wadanda hare-haren suka rutsa dasu yara ne.
(last modified 2018-08-22T06:57:47+00:00 )
Feb 10, 2016 08:27 UTC
  • wani sojan kamaru a arewa mai nisa
    wani sojan kamaru a arewa mai nisa

Akasarin wadanda hare-haren suka rutsa dasu yara ne.

Rahotanni daga kamaru na cewa mutane shida ne suka rasa rayukan su, a wasu jerin hare-haren kunar bakin wake a kwauyan Nguetchewe dake yankin arewa mai nisa na kasar.

Hare-haren da aka kai a wannan kauyen dake kan iyaka da Najeriya sun kuma sanadin jikkata wasu mutane akalla 30 a cewar wasu majiyoyin tsaro.

An dai kai harin ne kan wasu masu zaman makoki a kauyen inda wasu bayanai ke cewa wadanda suka jikkatan zasu iya kai 50.

kawo yanzu babu wata kungiya data dau alhakin kai wadanan hare-haren, aman so tarin yawa akan danganta su da kungiyar nan da aka fi sani da Booko Haram.