-
MDD Ta Yi Maraba Da Tattaunawar Siyasa A Burundi
May 29, 2016 01:08MDD tayi maraba da tattaunawar siyasa da aka yi a kwanan baya a birnin Arusha dake arewacin kasar Tanzania kan rikicin siyasa kasar Burundi daya ki yaki cinyewa.
-
WHO ta goyi bayan a gudanar da Wasanin Olympic na RIO
May 28, 2016 06:41Kungiyar Lafiya ta Duniya ta ce Cutar Zika ba za ta hana a soke ko kuma sauya wurin wasannin Olympic din ba a kasar Brazil
-
Putin Ya Ce Ba Za Su Bar Kasar Siriya Ta Zama Kamar Kasashen Libiya Da Somaliya Ba
May 28, 2016 01:10Shugaban kasar Rasha ya bayyana cewa; Ba zasu taba zuba ido su kyale masu mummunar aniya su cimma burinsu na ganin kasar Siriya ta zame kamar yadda kasashen Libiya da Somaliya suka kasance a halin yanzu ba.
-
Ban Ki-Moon Ya Jaddada Muhimmancin Zama Tsakanin Gwamnati Burundi Da 'Yan Adawar Kasar
May 28, 2016 01:08Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya jaddada muhimmancin gudanar da zaman tattaunawa na kai tsaye tsakanin gwamnatin Burundi da 'yan adawar kasar.
-
Obama ya Ziyarci Hiroshima
May 27, 2016 13:43Shugaban Amurka Barack Obama ya ziyarci birnin Hiroshima na kasar Japan, wanda Amurka ta kai wa hari da makamin nukiliya a lokacin yakin duniya na biyu.
-
An Samu Tashin Farashin Mai A Kasuwar Mai Ta Duniya
May 27, 2016 00:41Rahotanni sun bayyana cewar a karon farko a shekarar 2016 an sami tashin farashin man fetur zuwa dalla 50 kan kowace gangar danyen man hakan kuwa ya biyo bayan yawaitar bukatarsa ne a kasashen duniya.
-
Gwamnatin Aljeriya Ta Bada Umurnin Rufe Gidajen Talabijin Da Dama A Kasar
May 26, 2016 13:36Fira ministan Aljeriya ya bada umurnin rufe gidajen talabijin musamman masu zaman kansu da dama a duk fadin kasar a karkashin sabon shirin da gwamnatinsa ta bullo da shi a fagen yada labarai.
-
Bakin Haure Da Dama Sun Halaka Sakamakon Nutsewar Kwalerkwalensu A Tekun Libiya
May 26, 2016 12:55Dakarun bada agajin gaggawa da suke sanya ido a gabar tekun kasar Italiya sun bada labarin mutuwar bakin haure da dama sakamakon kifewar kwalekwalensu a kusa da gabar tekun kasar Libiya.
-
An Kira yi Taliban Ta Afghanistan Da Ta Rungumi Zaman Lafiya
May 26, 2016 07:40Shugaban Jam'iyyar Hizbul-Islami ta Afghanistan, Gulbaddin Hikmater ya kirayi Taliban da ta rungumi zaman lafiya.
-
Paparoma Yayi Wata Ganawar Karfafa Alaka Da Shugaban Jami'ar Azhar Sheik Ahmad Tayyib
May 23, 2016 13:57Rahotannin daga fadar Vatican, helkwatar mabiya darikar Katolika ta duniya sun bayyana cewar Fafaroma Francis, shugaban mabiya darikar Katolikan yayi wata tattaunawa da shugaban jami'ar Al-Azhar ta kasar Masar Sheikh Ahmad Tayyib a fadar Vatican, domin kyautata alaka tsakanin manyan addinan biyu da kuma batun fada da ta'addanci.