Jun 02, 2016 06:34 UTC

A shirin na yau zamu leka Najeriya, inda shugaban kasar Muhammadu Buhari ya cika shekara guda kan karagar mulki, za'aji cewa kuma wata kotun musamen ta Afirka dake birnin Dakar ta zartas da hukuncin rai da rai ga tsohon shugaban kasar Chadi Hissen Habre, A kamaru kuwa hukumomin kasar ne suka tabbatar da bullar cutar mura tsuntsaye. kadan kenan daga cikin abubuwa da za'aji a cikin shirin

A shirin na yau zamu leka Najeriya, inda a wannan makon ne shugaban kasar Muhammadu Buhari ya cika shekara guda kan karagar mulkin kasar, har wa zakuji cewa a cikin wannan mako ne wata kotun musamen ta Afirka dake birnin Dakar na kasar Senegal ta zartas da hukuncin zama gidan yari na rai da rai ga tsohon shugaban kasar Chadi Hissen Habre.

A jamhuriya kamaru kuwa hukumomin kasar ne suka tabbatar da bullar cutar mura tsuntsaye.

Akwai ma wasu taren labaren da suka fi daukan hankali a nahiyar.

Da fatan za a kasance tare da mu.

Tags