Gwamnatin Libiya Ta Jaddada Bukatar Neman Dage Mata Takunkumin Sayan Makamai
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i17141-gwamnatin_libiya_ta_jaddada_bukatar_neman_dage_mata_takunkumin_sayan_makamai
Fira ministan gwamnatin hadin kan kasa a Libiya ya jaddada bukatar neman dage wa kasarsa takunkumin sayan makamai.
(last modified 2018-08-22T06:59:36+00:00 )
Jan 29, 2017 08:55 UTC
  • Gwamnatin Libiya Ta Jaddada Bukatar Neman Dage Mata Takunkumin Sayan Makamai

Fira ministan gwamnatin hadin kan kasa a Libiya ya jaddada bukatar neman dage wa kasarsa takunkumin sayan makamai.

A jawabinsa a zaman taron shugabannin kasashen Afrika da suke makobtaka da kasar Libiya a jiya Asabar: Fira ministan gwamnatin hadin kan kasa a Libiya Fayiz Assarraj ya jaddada yin kira ga kungiyar tarayyar Afrika da sauran kungiyoyin kasa da kasa kan su taimaka a hanzarta cire takunkumin da aka kakaba kan kasarsa na hanata sayan makamai.

Assaraj ya kara da cewa: Azamar da gwamnatin Libiya take da ita na ganin ta kawo karshen duk wani aikin ta'addanci a cikin kasarta lamari ne da ya dogara kan irin karfin makaman da take da shi.