Zaman Taron Kasashe Masu Makwabtaka Da Libya A Aljeriya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i20176-zaman_taron_kasashe_masu_makwabtaka_da_libya_a_aljeriya
Manzon musamman na majalisar dinkin duniya a kan rikicin kasar Libya ya bayyana cewa,a yau za a fara gudanar da zaman taron kasashe masu makwabtaka da kasar Libya a kasar Aljeriya.
(last modified 2018-08-22T11:30:04+00:00 )
May 08, 2017 07:30 UTC
  • Zaman Taron Kasashe Masu Makwabtaka Da Libya A Aljeriya

Manzon musamman na majalisar dinkin duniya a kan rikicin kasar Libya ya bayyana cewa,a yau za a fara gudanar da zaman taron kasashe masu makwabtaka da kasar Libya a kasar Aljeriya.

Kamfanin dillancin Sharq Al-ausat ya bayar da rahoton cewa, mazon musamman na majalisar dinkin duniya a kan rikicin Libya Martin Kobler ya fadi da jijjifin safiyar yau cewa, za a fara taron na yau ne a kasar Aljeriya, tare da halartar dukkanin kasashe masu makwabtaka da kasar Libya.

Ya ce babbar manufar taron dai ita ce tattauna hanyoyin samar da zaman lafiya mai dorewa  a kasar ta Libya, da kuma komawar dukkanin bangarorin siyasa na kasar a kan teburin tattaunawa tare da warware matsalolinsu ta hanyoyi na siyasa da fahimtar juna, wanda dukkanin bangarorin siyasar kasar da suka hada da Khalifa Haftar duk sun amince da hakan.