Bincike Kan Laifufukan Da Aka Yi Kan Bakin Haure A Libiya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i20206-bincike_kan_laifufukan_da_aka_yi_kan_bakin_haure_a_libiya
Kotun Hukunta manyan Laifuka ta kasa da kasa ta fara gudanar da bincike kan laifufukan da ake tabkawa kan 'yan gudun hijra a kasar Libiya
(last modified 2018-08-22T07:00:05+00:00 )
May 09, 2017 02:12 UTC
  • Bincike Kan Laifufukan Da Aka Yi Kan Bakin Haure A Libiya

Kotun Hukunta manyan Laifuka ta kasa da kasa ta fara gudanar da bincike kan laifufukan da ake tabkawa kan 'yan gudun hijra a kasar Libiya

Kamfanin dillancin Labaran kasar Faransa ya nakalto Fatou Bensouda Babbar mai shigar da kara a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya-ICC, a jiya Litinin na cewa akwai duban 'yan gudun hijra na kasashen Afirka dake cikin mawuyacin hali a gidagen kurkuku na kasar Libiya daga cikin su akwai Mata da kananen yara.

Uwar gida Fatou Bensouda ta kara da cewa fyade, kisa , azabtarwa ya zamanto ba laifi ba ga jami'an tsaron gidajen Yarin na kasar Libiya.

Yayin da take bayyani kan yanayin tsaro a kasar ta Libiya,Babbar mai shigar da kara a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya-ICC, Fatou Bensouda ta ja hankali kan alakar dake tsakanin masu safarar Mutane da kuma yadda wadannan kungiyoyi ke bunkasa tare da kungiyoyin 'yan ta'adda a kasar ta Libiya.

Tun bayan faduwar Gwamnati Kanar Mu'amar Kaddafi a shekarar 2011, masu safarar mutane ke mumunar amfani da wannan dama wajen safarar Mutane daga yammacin kasar ta hanyar ruwa zuwa kasar Italiya.