Feb 24, 2018 06:49 UTC
  • Hamas Ta Mayar Wa Amurka Martani Akan  Ofishin Jakadanci A Birnin Kudus

Kungiyar gwagwarmayar musulunci ta Hamas ta yi tir da karatowar lokacin mayar da ofishin jakadancin Amurkan zuwa birnin Kudus.

Kakakin kungiyar ta Hamas, Abdullatif al-Qanuu ya sanar da cewa; Matakin na Amurka na mai da  ofishin jakadancin nata daga Tel Avivi zuwa birnin Kudus, zai mai da haramtacciyar Kasar Isra'ila zama wacce al'ummar yankin gabas ta tsakiya za su kalubalanta.

Alqanuu ya ci gaba da cewa; Mayar da ofishin jakadancin Amurka zuwa Kudus ba zai bai wa haramtacciyar kasar Isra'ila halarci ba.

Kakakin na kungiyar Hamas ya kuma ce; Matakin yana cin karo da dokokin kasa da kasa.

A watan Disamba na 2017 ne shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar da aniyar gwamnatinsa na mayar da ofishin jakadancinta zuwa birnin kudus.

Tags