-
Rasha:'Yan Ta'adda Na Shirye-Shiryen Kai Hari Da Makamai Masu Guba A Idlib
Mar 16, 2019 05:22Ma'aikatar harakokin wajen Rasha ta sanar a jiya juma'a cewa 'yan ta'addar kungiyar Tahriru Sham na shirye-shiryen kai hari da makamai masu guba a birnin Idlib na kasar Siriya
-
Mogherini Ta Yi Allah Wadai Kan Harin Da Aka Masallatai Biyu A New-Zeland
Mar 15, 2019 16:53Babbar jami'a mai kula da harakokin siyasar wajen kungiyar tarayyar Turai ta yi Allah wadai kan harin ta'addancin da aka kai wasu masallatai biyu a kasar New-zeland.
-
Faransa: An karfafa Matakan Tsaro A Wuraren Ibadu.
Mar 15, 2019 16:52Ministan cikin gidan kasar Faransa ya bukaci sa ido da karfafa matakan tsaro a wuraren ibadu na fadin kasar gaba daya, bayan harin ta'addancin da aka kai masallatai biyu a kasar New-Zeland.
-
Faransa: Adadin Mutane Marassa Wurin Kwana Ya Kai 566
Mar 15, 2019 16:51Wasu alkalumma da cibiyoyin da suke da dangantaka da gwamnatin kasar Faransa suka fitar sun nuna cewa, adadin wadanda ba su da wurin kwana a kasar ya kai 566 a cikin shekara ta 2018 da ta gabata.
-
Kamfanin Boeing Ya Amince Ya Dakatar Da Ayyukan Jirginsa Samfurin 737 Max - 8
Mar 15, 2019 16:46Kamfanin kera jirage na Boeing na kasar Amurka ya amince ya dakatar da ayyukan jirginsa samfurin 737 Max - 8, biyo bayan hatsarin da ya auku da jirgin a kasar Ethiopia a cikin wannan mako.
-
Kwamitin Kare Hakkin Bil Adama Na EU Ya Bukaci A Yi Adalci kan kisan Khahsoggi
Mar 15, 2019 16:45Babban kwamitin kare hakkin bil adama na kungiyar tarayyar turai ya bukaci da a yi adalci kan batun kisan gillar da aka yi wa dan jaridar kasar Saudiyya Jamal Khashoggi.
-
Koriya Ta Arewa Na Tunanin Soke Tattaunawar Nukiliyarta Da Amurka
Mar 15, 2019 09:08Kasar Koriya ta Arewa ta ce tana tunanin dakatar da tattaunawar data fara da Amurka kan batun nukiliyarta, bayan da tattaunawa ta tsakanin shuwagabannin kasashen biyu ta watse ba tare da cimma wata matsaya ba.
-
New Zeland : Hare-Haren Ta'addanci Kan Masallatai Sun Yi Ajalin Musulmai 49
Mar 15, 2019 08:13Rahotanni daga New Zeland, na cewa mutum 49 ne suka rasa rayukansu, kana wasu ashirin na daban suka raunana a yayin wasu tagwayen hare haren bindiga da aka kai kan wasu masallatai biyu a yankin Christchurc.
-
Venezuela: An Koma Bakin Aiki Bayan Dawowar Wutar Lantarki A Yawan Yankuna
Mar 14, 2019 16:42A yau Alhamis an koma baki ayyuka a kasar Venezuela, bayan daukewar wutar lantarki na kusan mako guda a kasar, wanda ya yi sanadiyyar tsayawar harkoki da dama a kasar.
-
An Aike Da Bakaken Akwatuna Na Jirgin Ethipoia Da Ya Fadi Zuwa Faransa
Mar 14, 2019 16:35Kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na kasar Ethiopia ya aike da bakaken akwatuna biyu masu nadar bayanai na jirgin da ya fadi zuwa kasar Faransa.